Ba zan bari Matana, da ‘Yayana su shiga sha’anin mulki na ba – Abba Gida-Gida

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Zababben gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf (wanda aka fi sani da Abba Gida-Gida) na jam’iyyar NNPP ya ce matansa da ‘ya’yansa ba za su shiga sabgar mulkin da zai yi jihar kano ba.

 

Abba Kabir Yusuf, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi a wajen karbar takardar shaidar lashe zabe a ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta ke kano.

INEC ta baiwa Abba Gida-gida Shaidar lashe zaben gwamnan Kano

Zababben gwamnan ya ce ba zai bari ‘yan uwansa su yi wani tasiri a harkokin mulkin sa a lokacin gwamnatin sa ba, saboda ba tare suka yi rantsuwar kama aiki da shi ba.

 

“Mata na ba za su shiga harkokin mulkina ba. ‘Ya’yana ba za su shiga cikin harkokin mulki ba. Kuma zan iya baku tabbacin cewa haka shima mataimakina.” inji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...