Ba zan bari Matana, da ‘Yayana su shiga sha’anin mulki na ba – Abba Gida-Gida

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Zababben gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf (wanda aka fi sani da Abba Gida-Gida) na jam’iyyar NNPP ya ce matansa da ‘ya’yansa ba za su shiga sabgar mulkin da zai yi jihar kano ba.

 

Abba Kabir Yusuf, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi a wajen karbar takardar shaidar lashe zabe a ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta ke kano.

INEC ta baiwa Abba Gida-gida Shaidar lashe zaben gwamnan Kano

Zababben gwamnan ya ce ba zai bari ‘yan uwansa su yi wani tasiri a harkokin mulkin sa a lokacin gwamnatin sa ba, saboda ba tare suka yi rantsuwar kama aiki da shi ba.

 

“Mata na ba za su shiga harkokin mulkina ba. ‘Ya’yana ba za su shiga cikin harkokin mulki ba. Kuma zan iya baku tabbacin cewa haka shima mataimakina.” inji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...