‘Ƴan Najeriya za su yi kewar Buhari idan ya sauka daga mulki – Garba Shehu

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Babban mai bai wa Shugaban Najeriya shawara kan kafafen yaɗa labarai, Mallam Garba Shehu ya koka kan irin caccakar da ake yi wa shugaban ƙasar, Muhammadu Buhari.

 

Ya ce ba a nuna ƙauna ga shugabanni a lokacin da suke mulki.

 

Saudiyya ta gargaɗi masu ɗaukar hoto a lokacin ziyarar ibada

Ya bayar da misali da zamanin mulkin Goodluck Jonathan wanda ya ce mutane sun yi ta sukarsa amma a yanzu, ya zama mutumin da ƴan Najeriya da dama ke yabo.

INEC ta saka ranar ƙarasa zaɓukan da ba a kammala ba

 

Mallam Garba Shehu ya ce irin haka za ta faru idan Buhari ya miƙa mulki ga shugaban ƙasa na gaba.

 

Game da manufar taƙaita amfani da garin kuɗi, Garba Shehu ya ce tsarin na gwamnati mai ci abin so ne a don haka ba za a soke shi ba.

 

A cewarsa, “taƙaita amfani da takardun kuɗi ci gaba ne ga ƴan Najeriya saboda ƙasashen da suka ci gaba tuni suke tafiya a kan wannan tsarin”.

 

Al’ummar Najeriya sun yi ta fuskantar matsaloli saboda ƙaranvin takardun kuɗi tun bayan da gwamnati ta bijiro datsarin sauya fasalin takardun kuɗin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...