Karancin kuɗi: Gwamnan CBN ya nemi afuwar yan Nigeria

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Gwamnan Babban Bankin Najeriya Godwin Emiefele, ya roki afuwar ƴan Najeriya kan matsalar da ake fuskanta wajen tura kuɗi ta intanet. Kwamitin tsare-tsare kan harkar kuɗi

Emefiele ya bayyana haka ne a taron kwamitin tsare-tsare kan harkokin kuɗi da aka gudanar a Abuja, inda ya tabbatar wa ƴan ƙasar cewa za a magance matsalar nan ba da jimawa ba.

A cewarsa, sashin da ke kula da biyan kuɗaɗe na babban bankin, ya yi iya kokarinsa don tabbatar da cewa an magance matsalar, a daidai lokacin da ƴan Najeriya ke ci gaba da fuskantar wahalhalu wajen aika kuɗi da wayoyinsu da kuma a na’urar cirar kuɗi ta POS.

An soma fuskantar matsalar ne tun bayan da gwamnati ta kaddamar da batun sake fasalta kuɗi wanda kuma ya janyo ƙarancin takardun kuɗi a faɗin ƙasar.

“Dole mu bai wa ƴa Najeriya hakuri. Mutane na cikin wahala kan rashin samun aika kuɗi ta intanet. Amma ina ganin ana kokarin shawo kan matsalar,” in ji Emiefiele.

A taron, gwamnan babban bankin ya kuma yi magana kan rashni wadatuwar takardun kuɗi a ƙasar saboda sake fasalin naira, inda ya ce bankin zai ci gaba da buga sabbin takardun kuɗi domin su wadatu musamman ma a kasuwanni

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...