Ina da kyakyawar dangantaka da Shekarau, Kwankwaso da Ganduje – Gawuna

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Mataimakin gwamnan jihar Kano kuma dan takarar gwamna na jam’iyyar APC Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya bayyana cewa yana da kyakyawar dangantaka da dakkanin gwamnonin da ya yi aiki da su a kano .

 

A cewarsa…“Ina da kyakkyawar alaka da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje da sauran tsofaffin Gwamnonin da na yi aiki da su a gwamnatocin baya a matsayin da Shekarau da nayi aiki da shi a matsayin shugaban karamar hukuma, da kuma Kwankwaso da nayi masa kwamishina da kuma a yanzu a matsayina na Mataimakin Gwamna Ganduje, duk kuwa da bambancin jam’iyyar siyasa.

 

Gawuna ya bayyana hakan ne yayin da ya tattaunawa da shi a cikin wani shiri na gidan talabijin din TVC mai suna “Countdown Nigeria Decides 2023″.

 

Ya kuma kara da cewa bai yarda a samu gaba ko hatsaniya tsakanin yan Siyasa a Kano ba , kawai kamata yayi mufi fifita jihar kano fiye da son kanmu”.

 

Ban ce a zabi wani dan takarar gwamnan kano da ba Abba Gida-gida ba – Sen. Kawu Sumaila

A cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran mataimakin gwamna Hassan Musa Fagge ya aikowa kadaura24, yace  dan takarar gwamna na jam’iyyar APC ya bukaci al’ummar Kano da su yi la’akari da kwarewa da amincin ‘yan takara a matsayin ma’auni yayin kada kuri’a.

 

“Ina da kwarewar da ake bukata a harkokin mulki wanda ya sanya ni a saman duk sauran ‘yan takarar gwamna” Gawuna ya bayyana”.

 

Yadda wasu kananan hukumomi suka tafka babbar asara sanadin takarar Kwankwaso – Ra’ayin Aminu Dahiru

Ya kuma nanata bayar da ‘yancin cin gashin kai ga kananan hukumomin jihar idan aka zabe shi a matsayin Gwamnan kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...