Obasanjo ba shi da ƙimar da zai nemi a soke zaɓe – Gwamnatin Najeriya

Date:

Gwamnatin Najeriya ta ce tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ba shi da “wata kimar” da zai nemi a dakatar da tattara sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da ake yi yanzu haka a ƙasar.

Gwamnatin ta mayar masa da martani ne bayan wasiƙar da ya rubuta a yammacin Litinin, yana mai neman Shugaba Muhammadu Buhari da shugaban hukumar zaɓe Mahmood Yakubu su soke sakamakon wasu yankuna da ya yi zargin cewa na yi maguɗi.

Da yake mayar da martani, Ministan Yaɗa Labarai da Al’adu, Lai Mohammed ya zargi tsohon shugaban da gudanar da zaɓe “mafi muni a tarihin dimokuraɗiyyar Najeriya”.

“Duk da cewa yana bayyana kansa a matsayin dattijo mai kishin ƙasa, an san Obasanjo da goyon bayan wata jam’iyya da kuma yaudarar ‘yan Najeriya ta hanyar tauye musu abin da suka zaɓa,” kamar yadda wata sanarwa daga ma’aikatar yaɗa labarai ta ambato ministan na cewa.

Obasanjo ya ce ba wani sabon abu ba ne a zargi wasu daga cikin ma’aikatan hukumar zaɓen da suka gudanar da aikin da karɓar cin hanci kafin aika sakamako ta hanyar na’ura, abin da ya sa ake zargin an ƙirƙiri wani sakamkon ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: Bam ya fashe a Kano ya hallaka wasu ya kuma jikkata wasu

Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin...

Kotu a Kano ta sami wani Tela da laifin takurawa makwabtansa da karar keken dinki

Wata kotu a Kano ta samu wani tela da...

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...