Kabiru Gaya ya Magantu, bayan bayyana sakamakon Zaɓen kano ta kudu

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Sanatan kano ta kudu Kabiru Ibrahim Gaya ya bayyana cewa ya karbi sakamakon zaɓen dan majalisar Dattawa na shiyyar Kano ta kudu da aka gudanar wanda ya bayyana Hon. Sulaiman Abdulrahman Kawu Sumaila na jam’iyyar NNPP nasara.

Sanata Kabiru Gaya ya bayyana hakan ne cikin wani sakon murya da aka aikowa kadaura24 da yammacin ranar litinin din.
Kabiru Gaya ya kuma taya Kawu Sumaila Murnar lashe zaben, tare da bashi tabbacin ba zai ƙalubalanci sakamakon zaben a kotu ba.
” Sau hudu na ci zaben sanatan kano ta kudu Kuma a cikin hudun nan sau daya kawai aka taba kai ni kara kotu sauran 3 ba’a kaini ba, don haka ina sanar da kawu Sumaila cewa ba zan Kai shi Kara kotu ba Kuma ina taya shi murna”. Inji Sanata Kabiru Gaya
Sanata wanda yayi Sanatan kano ta kudu sau hudu ya godewa daukacin al’ummar yankin wadanda suka hadar da yan kasuwa Dattawa mata da matasa bisa hadin kan da suka bashi tsahon shekaru 16.
Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a safiyar Litinin din nan ne hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta aiyana Hon. Kawu Sumaila na jam’iyyar NNPP a matsayin sabon Sanatan kano ta kudu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: Bam ya fashe a Kano ya hallaka wasu ya kuma jikkata wasu

Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin...

Kotu a Kano ta sami wani Tela da laifin takurawa makwabtansa da karar keken dinki

Wata kotu a Kano ta samu wani tela da...

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...