Ahmad Lawan ya sake lashe zaben Sanatan Yobe-ta-Arewa

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmed Lawan na jam’iyyar All Progressives Congress, APC, ya lashe zaben Sanatan Yobe-ta-Arewa a Yobe.

 

Da ya ke bayyana sakamakon zaben a Gashua a yau Litinin, jami’in zaben, Farfesa Omolala Aduoju na jami’ar tarayya, Gashua, ya ce Lawan ya samu kuri’u dubu 91,318.

 

“Bayan cika sharuddan doka kuma ya samu mafi yawan kuri’u, an bayyana Alhaji Ahmed Lawan na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben kuma aka dawo zabe,” inji shi.

 

Ya ce babban abokin hamayyar Lawan, Sheriff Abdullahi, na jam’iyyar PDP, ya zo na biyu da kuri’u 22,849, yayin da ɗan takarar jam’iyyar New Nigerian Peoples Party, NNPP, Garba Umar, ya samu kuri’u 7,210.

 

Mista Aduoju ya ce jam’iyyar Action Democratic Party, ADP ta samu kuri’u uku duk da cewa jam’iyyar ba ta tsayar da dan takara a zaben ba.

 

“Jimillar kuri’un da aka kada a zaben sun kai dubu 126,677 daga cikinsu 122,136 sun yi aiki kuma an ki kuri’u 4,541,” inji shi.

 

Gundumar ta ƙunshi kananan hukumomin Machina, Nguru, Bade, Karasuwa, Jakusko da Yusufari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dr. Kabiru Getso Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Buhari

Daga Rahama Umar Gwaru   Tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli...

Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutu saboda rasuwar Buhari

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana Talata, 15 ga watan...

Injiniya Iliyasu Usman Salihu ya zama Jakadan zaman Lafiya na Africa

    Injiniya Ilyasu Uasman Salihu, Manajan Darakta na Sadex Engineering...

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...