Hukumar ICPC mai binciken laifukan cin hanci da rashawa a Najeriya ta ce ta kama mutum tara saboda laifin sayen ƙuri’u a jihohi biyar na Najeriya.
ICPC ta kama mutanen ne lokacin gudanar da babban zaɓen shugaban ƙasa da na ƴan majalisar dokoki a jihohin Osun da Ondo da Borno da Akwa Ibom da Sokoto.
A cewar hukumar, kamar yadda ta wallafa a shafinta na Tuwita, an kama mutum huɗu masu sayen ƙuri’u a jihar Osun, biyu a jihar Sokoto sai kamen da ICPC ta yi a Ondo da Akwa Ibom da Borno inda aka kama mutum ɗaya kowace jiha.
Zuwa yanzu dai hukumar ta ce mutanen da aka kama a Osun na tsare a ofishinta da ke jihar kuma an same su ne da wasu takardu ɗauke da sunaye da kuma lambobin wayoyinsu har da bayanan asusun ajiyar bankinsu.