Zaben Shugaban Kasa: NNPP A Kano ta fitar da sanarwa ta musamman

Date:

 

 

Sanarwa ta Musamman

 

Bayanan sirrin da muka samu sun tabbatar da cewa gwamnatin jahar Kano da jam’iyyar APCmaimulki sun tanadi ‘yan daba a wurare daban daban da niyyar tada tarzoma bisa ganin alamun nasarar jam’iyyar mu ta NNPP a zaben da ya gudana yau Asabar.

 

A saboda haka, muke kira ga hukumomin tsaro da su kara zage damtse wajen kare lafiyar ma’aikatan zabe, masu sa idanu akan zabe da wakilan jam’iyyu da kuma al’ummar jahar Kano baki daya.

 

A bisa wannan dalili, muna shawartar dukkanin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar NNPP da su tsaya tsayin daka don tabbatar an kidaya dukkanin kuri’un da aka kada tare shigar da sakamako cikin na’urar da hukumar zabe ta tanadar sannan kuma a tabbatar ta an bayyana sakamakon kamar yadda dokar zabe ta 2022 ta tanadar.

 

Sanusi Bature Dawakin Tofa

Maimagana da Yawun Kwamatin Yakin Neman Zabe na Jam’iyyar NNPP Reshen Jahar Kano a Shekara ta 2023

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...