Sanarwa ta Musamman
Bayanan sirrin da muka samu sun tabbatar da cewa gwamnatin jahar Kano da jam’iyyar APCmaimulki sun tanadi ‘yan daba a wurare daban daban da niyyar tada tarzoma bisa ganin alamun nasarar jam’iyyar mu ta NNPP a zaben da ya gudana yau Asabar.
A saboda haka, muke kira ga hukumomin tsaro da su kara zage damtse wajen kare lafiyar ma’aikatan zabe, masu sa idanu akan zabe da wakilan jam’iyyu da kuma al’ummar jahar Kano baki daya.
A bisa wannan dalili, muna shawartar dukkanin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar NNPP da su tsaya tsayin daka don tabbatar an kidaya dukkanin kuri’un da aka kada tare shigar da sakamako cikin na’urar da hukumar zabe ta tanadar sannan kuma a tabbatar ta an bayyana sakamakon kamar yadda dokar zabe ta 2022 ta tanadar.
Sanusi Bature Dawakin Tofa
Maimagana da Yawun Kwamatin Yakin Neman Zabe na Jam’iyyar NNPP Reshen Jahar Kano a Shekara ta 2023