Ku Karbi Kaddara Idan Kuka Fadi Zabe – Buhari ya fadawa yan takarar shugaban kasa

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Shugaba Muhammadu Buhari ya buƙaci dukkan ‘yan takarar kujeru daban-daban a babban zaɓen ƙasar da ke tafe a ranar Asabar da su mutunta ‘yancin masu zaɓe da kuma karɓar sakamakon zaɓen da hannu biyu.

Buhari na magana ne a Abuja jiya Laraba, yayin wani taro da Kwamitin Zaman Lafiya na Ƙasa ya shirya domin ganin jam’iyyu da ‘yan takarar kujerar shugaban ƙasa sun sa hannu na yarjejeniyar yin zaɓe lafiya.

Talla

Shugaban Najeriyar ya kuma buƙaci wadanda suka ki karɓar sakamakon zaɓen da su bi kadinsu ta hanyar shari’a.

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

“Ina kira ga dukkan ‘yan takara na kujeru daban-daban a wannan zaɓe da su tabbata sun mutunta ‘yancin masu zaɓe da kuma karɓar sakamakon zaɓe da hukumar zaɓe za ta sanar, wanda sune dka ta bai wa damar yin hakan,” in ji Buhari.

Shugaban ya kuma yaba wa kwamitin zaman lafiya na ƙasa, inda ya ce duk da cewa babu wani taimako na kuɗi da gwamnati ke bai wa kwamitin, ta dai ci gaba da aiki da hukumomi daban-daban domin ganin abubuwa sun tafi daidai da kuma ƙoƙari wajen shiga tsakani kan sha’anin zaɓe.

Shugaba Buhari ya ce yana sane da damuwa da ake nunawa kan yadda za a gudanar da zaɓen da kuma yadda abubuwa za su kasance bayan bayyana sakamakon zaɓen.

Ya ce tun zuwa kan mulki, gwamnatinsa ta yi aiki tukuru wajen tabbatar da ta bar abin tarihi na gudanar da zaɓe cikin gaskiya da adalci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...