An kama malamin jinya kan zargin yi wa marasa lafiya fyaɗe

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

‘Yan sandan Uganda sun kama wani malamin jinya kan zargin yunkurin yi wa wasu mata masu ciki biyu fyaɗe a wani asibitin gwamnati mai suna Entebbe da ke da nisan kilomita 40 da Kampala, babban birnin ƙasar.

 

Mataimakin mai magana da yawun ‘yan sandan birnin, Luke Owoyesigire, ya ce an kama wanda ake zargin ne mai suna Kutesa Denis a jiya Lahadi kuma yana tsare a ofishin ‘yan sanda da ke Entebbe.

Talla

Ana zargin cewa sai da Kutesa ya bai wa matan biyu da ke sashin kula da mata na asibitin wani kwayar magani suka sha kafin ya ci zarafinsu.

 

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

An kuma gano wasu kwayoyi a gidansa bayan gudanar da bincike da kuma wata takarda da ake zargin ya rubuta inda yake rokon a yi masa addu’a kan abin da yake fuskanta mara kyau a yawan lokuta.

 

‘Yan sanda sun ce akwai yiwuwar ƙarin wasu da aka ci wa zarafi, inda suke buƙatar mutane su fito su yi magana.

 

Darektan asibitin, Dakta Peterson Kyebambe ya faɗa wa BBC cewa lamarin ya sanya yanzu sun fara saka ido kan likitoci da ma’aikata ko kuma kafa kyamarorin tsaro a faɗin asibitin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...