Yan jam’iyyar PDP  sama da 10,000 ne suka sauya sheka zuwa NNPP a Kano

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria
 Kwanaki shida kafin gudanar da babban zaben kasa, shugabannin jam’iyyar PDP reshen jihar Kano sun koma jam’iyyar NNPP .
 A wani gagarumin gangami da aka gudanar, shugaban jam’iyyar NNPP na kasa Farfesa Rufa’i Ahmed Alkali tare da mataimakin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Bishop Isaac Idahosa ne suka tarbi wadanda suka sauya shekar a Kano .
Talla
 Shugabannin jam’iyyar PDP karkashin jagorancin shugaban jam’iyyar na jiha Alhaji Shehu Wada Sagagi sun yanke shawarar ficewa daga jam’iyyar ne, sakamakon rashin tafiyar da tsarin dimokuradiyya a cikin jam’iyyar da kuma son zuciya da shugabannin jam’iyyar na kasa suke yi.
Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil
 Da yake jawabi a wajen taron, Shehu Sagagi ya ce shi kan sa tare da shugabannin kwamitin zartarwar jam’iyyar PDP na jihar Kano su 36, shugabannin kananan hukumomi sama da 700, shugabannin mazabu sama da 8,000, wakilan jam’iyyar na kasa 44 da kuma wakilan mazabu 1,452 ne suka shiga jam’iyyar NNPP.
 “Siyasa magance ta yawa , muna kyautata zaton Sen. Rabiu Musa Kwankwaso zai kai mu ga nasara tun daga matakin kasa har jiha” in ji Sagagi.
 Ya kuma zargi jam’iyyar PDP da yiwa kanta zagon kasa a jihohi kamar Kano ta hanyar barin irin su Sanata Kwankwaso su fice daga jam’iyyar duk da dimbin mabiyansu ba a jihar kadai ba har ma da kasa baki daya.
 A wata sanarwa da Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben NNPP a jihar Kano, ya an bato shugaban NNPP na kasa yana taya sabbin wadanda suka sauya sheka murnar shiga jam’iyyar NNPP.
 A martanin da ya yi, mataimakin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP Bishop Isaac Idahosa ya tarbi wadanda suka sauya shekar cikin farin ciki, yana mai cewa da wannan gaggarumin sauya sheka mai cike da tarihi, NNPP za ta yi nasara a zabe mai zuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...