2023: Jam’iyyu 5 sun narke don mara wa Atiku baya a zaɓe mai zuwa

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Gabanin zaben 2023, biyar daga cikin jam’iyyun siyasa 18 a Nijeriya sun amince da mara wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar baya.

 

Jam’iyyun biyar sun bayyana hakan ne a babban taron gangamin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP da aka gudanar a dandalin Mahmud Ribadu, da ke Yola, babban birnin jihar Adamawa a yau Asabar.

Talla

Jam’iyyun dai sun hada da Allied Peoples Movement, African Democratic Congress, National Rescue Movement, Action Alliance da Action Peoples Party.

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

 

Shugaban gamayyar jam’iyyun, APM na kasa, Yusuf Dantalle, wanda ya yi magana a madadin jam’iyyun ne ya bayyana hakan.

A ranar Juma’a ne shugaban jam’iyyar APM na kasa ya amince da takarar Atiku a madadin ƴar takarar shugaban kasa mace daya tilo a jam’iyyar APM, a zaben shugaban kasa na 2023, Chichi Ojei.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...