2023: Jam’iyyu 5 sun narke don mara wa Atiku baya a zaɓe mai zuwa

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Gabanin zaben 2023, biyar daga cikin jam’iyyun siyasa 18 a Nijeriya sun amince da mara wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar baya.

 

Jam’iyyun biyar sun bayyana hakan ne a babban taron gangamin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP da aka gudanar a dandalin Mahmud Ribadu, da ke Yola, babban birnin jihar Adamawa a yau Asabar.

Talla

Jam’iyyun dai sun hada da Allied Peoples Movement, African Democratic Congress, National Rescue Movement, Action Alliance da Action Peoples Party.

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

 

Shugaban gamayyar jam’iyyun, APM na kasa, Yusuf Dantalle, wanda ya yi magana a madadin jam’iyyun ne ya bayyana hakan.

A ranar Juma’a ne shugaban jam’iyyar APM na kasa ya amince da takarar Atiku a madadin ƴar takarar shugaban kasa mace daya tilo a jam’iyyar APM, a zaben shugaban kasa na 2023, Chichi Ojei.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...