2023: Jam’iyyu 5 sun narke don mara wa Atiku baya a zaɓe mai zuwa

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Gabanin zaben 2023, biyar daga cikin jam’iyyun siyasa 18 a Nijeriya sun amince da mara wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar baya.

 

Jam’iyyun biyar sun bayyana hakan ne a babban taron gangamin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP da aka gudanar a dandalin Mahmud Ribadu, da ke Yola, babban birnin jihar Adamawa a yau Asabar.

Talla

Jam’iyyun dai sun hada da Allied Peoples Movement, African Democratic Congress, National Rescue Movement, Action Alliance da Action Peoples Party.

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

 

Shugaban gamayyar jam’iyyun, APM na kasa, Yusuf Dantalle, wanda ya yi magana a madadin jam’iyyun ne ya bayyana hakan.

A ranar Juma’a ne shugaban jam’iyyar APM na kasa ya amince da takarar Atiku a madadin ƴar takarar shugaban kasa mace daya tilo a jam’iyyar APM, a zaben shugaban kasa na 2023, Chichi Ojei.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...