2023: Ni na jagorancin yin dokar da zata hana magudin zabe a Nigeria – Sanata Kabiru Gaya

Date:

Daga Abdulrashid B Imam

Sanatan kano ta kudu Art Kabiru Ibrahim Gaya ya a bayyana cewa a matsayin sa na shugaban kwamitin harkokin zabe a zauren majalisar Dattawa ta kasa shi ne ya jagoranci yin dokar data magance magudin zabe a Nigeria.
Kadaura24 ta rawaito Sanata Kabiru Gaya ya bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi a garin Sumaila lokacin da ya shiga garin domin bada tallafin jari ga matane 1000 a karamar hukumar.
Talla
Sanata Kabiru Gaya yace a wannan karon wadanda suka Saba satar akwatu a wajen zabe a wannan karon baza su iya yin hakan ba , saboda Sabbin dokokin da sukai wadanda suka magance yin magudin zabe.
Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil
” Idan mutum ya saba zuwa Wajen zabe ya saci akwatu to a wannan karon ba jar hula ba ko me ka Saka akan ka, zaka ka iya yin abun da ka saba ba, don haka ina baku tabbacin idan kuka sake zabe ne zan karasa muku aiyukan da an fara yi a Wannan karamar hukumar ta Sumaila”. Sanata Kabiru Gaya
Sanata Gaya ya kuma ce yanzu haka ya kashe Samar da naira Miliyan 500 domin samar da wani gidan ruwa a hayin gada wanda idan aka kammala shi , zai kawo ƙarshen duk wata matsalar ruwa a karamar hukumar Sumaila.
” Wadancan magudan kuɗade har Naira Miliyan dari biyar da na kashe Wajen gina rijiyoyin burtsatse da manyan tankuna da Kuma sola-sola da muka Saka , zan kara kashe naira Miliyan 150 domin kammala aikin, don haka ku zabi jam’iyyar APC a Rana ita yau domin na sami damar karasa muku aikin ta yadda ruwa zai shiga kowanne gida a karamar hukumar Sumaila “. A cewar Sanata Gaya

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...