INEC ta bayyana matakan da za a bi don kada kuri’a a ranar zabe

Date:

Daga Auwalu Alhassan Kademi

 

Hukumar Zaɓe mai zaman Kanta a Najeriya INEC ta bayyana matakan da za a bi domin kaɗa ƙuri’a a ranar zaɓe.

 

A wani saƙo da hukumar ta wallafa a shafinta na Tuwita ta bayyana matakai bakwai da ta ce za a bi domin kaɗa ƙuri’a ranar zaɓen.

Talla

A ranar 25 ga watan Fabrairun da muke ciki ne dai za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun dokokin ƙasar.

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Matakin farko shi ne lokacin fara zaɓen wanda hukumar ta ce zai fara da misalin ƙarfe 8:30 na safe.

 

Mataki na biyu shi ne gabatar da katin zaɓe ga jami’an zaɓe domin tantance shi ta hanyar amfani da na’urar BVAS.

 

Daga nan sai a duba ko sunan mutum na cikin rajistar masu kaɗa ƙuri’a a wannan rumfar zaɓen.

 

Mataki na gaba shi ne na’urar BVAS za ta tantance mutum ta hanyar saka ɗan yatsarsa a jikinta, daga nan sai a bai wa mutum ƙuri’ar da zai kaɗa.

 

Sai matakin kaɗa ƙuri’a wanda hukumar ta ce ta ware wuri na musamman da za a shiga domin kaɗa ƙuri’ar a asirce.

 

Matakin ƙarshe shi ne bayan kaɗa ƙuri’a mutum zai bar rumfar zaɓen, ko ya yi nesa da rumfar zaɓen na akalla mita 300.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...