Zamu gudanar da zaben 2023 kamar yadda aka tsara – Farfesa Mahmoud Yakubu

Date:

Daga Abdullahi  Shu’aibu Hayewa

 Farfesa Mahmood Yakubu, Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ya ce zaben 2023 zai gudana kamar yadda aka tsara.
 Farfesa Yakubu ya bayyana haka ne a ranar Laraba a Abuja lokacin da yake amsa tambayoyinb manema labarai, bayan ya yi wa Majalisar Zartarwa ta kasa, bayani kan matakin shirye-shiryen gudanar da zaben.
 Ya bayyana karancin man fetur da sake fasalin kudin Naira a matsayin manyan kalubalen da ke fuskantar INEC, ya ce duk da haka sun riga sun sami mafita akan haka .
Talla
 “Mun sanar da ‘yan majalisar zartarwar dukkan shirye-shiryen da muka yi na gudanar da zabukan da kuma ‘yan kalubalen da muke fuskanta da kuma matakan da muka dauka domin magance su.
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil
Farfesa Yakubu ya kara da cewa: “Don haka, mun fito da wadannan kalubale kuma mun samo hanyoyin magance wadannan kalubalen don haka muna bada tabbacin zamu gudanar da zaben kamar yadda aka tsara; a ranar 25 ga Fabrairu don zaben kasa da kuma ranar 11 ga Maris don zaben Jiha.”
 Shugaban na INEC ya kuma ce akwai shirin yiwa majalisar zartarwar bayani a ranar 10 ga watan Fabrairu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...