Sojoji sun kubutar da Mutane 18 da akai safarar su daga Kano

Date:

Rundunar sojin ruwa ta Najeriya ta kuɓutar da mutum 18 da aka yi safarsu a unguwar Rijiyar Lemu da ke ƙaramar hukumar Ungogo a jihar Kano da ke arewacin Najeriya

 

A wani saƙo da rundunar ta wallafa a shafinta na Facebook ta ce ta kama mutum biyu da take zargi da hannu wajen safarar mutanen.

 

Rundunar ta ce ta samu nasarar kuɓutar da mutanen ne bayan da wani jami’insu ya ankarar da su kasancewa ‘yar uwarsa na daga cikin mutanen da aka yi safar tasu.

 

Sojojin ruwan sun ce sun miƙa mutanen tare da waɗanda ake zargin hannun hukumar da ke yaƙi da safarar bil-adama ta ƙasar domin ɗaukar mataki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...