Chanjin kuɗi: Ya kamata Buhari ya duba wahalar da talakawa suke ciki – Samarin Tijjaniyya

Date:

An bukaci shugaba Muhammadu Buhari ya duba irin wahalar da talakawan kasar nan suke ciki kan canza fasalin kudaden kasar na 200 da 500 da 1,000.

 

Kadaura24 ta rawaito Kungiyar Samarin Tijjaniyya ta kasa ita ce tayi wannan Kiran a wata sanarwa mai dauke dasa hannun Sakataren Kungiyar na kasa Shehu Tasi’u Ishaq.

 

Sanarwar tace bisa la’akari da kuracewar wa’adin da Babban bakin kasa ya bayar na daina amfani da kudaden da aka sauya musu fasali ya janyo shiga halin kakanikayi ga talakawan kasar nan.

 

Kazalika al’uma sun shiga halin matsi da yunwa da fatara wanda hakan ka iya haifar da mummunar rayuwa ga alumar kasar nan.

Talla

A Don hakane kungiyar Samarin Tijjaniyar tayi kira da babbar murya ga shugaba Buhari ya duba wannan hali da al’umar kasar nan ke ciki, kuma ya tuna cewa talakawa ne suka tsaya tsayin daka wajan tabbatar dashi a matsayin da yake akai.

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Daga nan sai Kungiyar ta bukaci shugaba Buhari da ya umarci babban Bankin kasa wato Centarl Bank ya Kara wa’adin yin amfani da tsofaffin kudaden domin al’uma su samu damar shigar da wadanda suke hannunsu a bankuna

 

Haka kuma sanarwar ta bukaci al’umar wannan kasa su kwantar da hankulansu tareda cigaba dayin addu’ar samun sassauci a cikin wannan lamari domin samun ingantacciyar rayuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...