Majalisa za ta umarci ‘yan sanda su kamo Gwamnan babban bankin Nigeria

Date:

Daga Abdulrashid B Imam

 

Kakakin majalisar wakilan Najeriya Femi Gbajabiamila ya ce ba zai yi kasa a gwuiwa ba wajen neman Sufeto-Janar na ‘yan sandan Najeriya Usman Baba ya fitar da sammacin kama Godwin Emefiele, wanda shi ne gwamnan babban bankin kasar.

 

Wannan gargadin ya biyo bayan kin bayyana gaban majalisar a dalilin gayyatar da ta mika wa gwamnan. Mista Gbajabiamila ya sanar da haka ne a ranar Alhamis bayan da Alhassan Doguwa, shugaban masu rinjaye na majalisar ya gabatar da rahoton kwamitin majalisar bincike kan ayyukan banki na kasar.

Talla

Alhassan Doguwa ya sanar da majalisar cewa Mista Emefiele bai bayyana a gaban kwamitin ba kamar yadda aka bukace shi yayi a ranar Laraba.

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

A nasa bayanin da ya gabatar, Mista Gbajabiamila ya ce a shirye yake ya yi amfani da sashe na 89(1)(d) na kundin tsarin mulkin Najeriya wanda ya ba majalisa ikon umartar jami’an tsaro su kamo wanda ya ki bayyana a gaban majalisar.

 

Sai dai Mista Emefiele ya bayyana cewa matsalar da aka kira shi akai ta karancin sababbin takardun kudi ce, kuma alhakin haka ya rataya ne a wuyan bankunan kasuwanci na kasar.

 

Ya kuma kafe cewa ba zai tsawaita kwanakin da bankin ya tanadar wa ‘yan Najeriya su sauya tsofaffin takardun kudinsu da sababbin ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...