An maka wani mai gidan haya a kotu bisa yage kwanon rufin ƴan-haya

Date:

Daga Abdullahi Danbala Gwarzo

 

A yau Alhamis ne wata mai gidan haya mai suna Temitope Olayiwola mai shekaru 45 da ta cire rufin gidan ƴan haya, ta gurfana a gaban wata babbar kotun majistare ta Sabo-Yaba da ke Legas.

 

Olayiwola da ke Plot na 15 a rukunin gidaje na Oyadiran, Sabo-Yaba, Legas, ta musa laifuka biyu da ake tuhumar ta da su na rashin zaman lafiya da lalata da gangan.

 

Mai gabatar da kara, SP. Thomas Nurudeen, ya shaida wa kotun cewa Olayiwola ta aikata laifin ne a ranar 10 ga watan Disamba, 2022, a Plot 15 Oyadiran Estate, Sabo-Yaba, Legas.

Talla

Ya yi zargin cewa Olayiwola da gangan ta cire rufin kwanon na Edem Yves da Evans Anyanwu, wadanda ke haya a gidanta.

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Nurudeen ya bayyana cewa Olayiwola ta dauki matakin lalata rufin gidajen ne bayan da ta yi yunkurin biyansu kudin haya.

 

A cewarsa, laifukan sun ci karo da tanadin sashe na 168 da 350 na dokokin laifuka na jihar Legas, na 2015.

 

Alkalin kotun, Mista Peter Nwaka, ya amince da bayar da belin Olayiwola a kan kudi N600,000 tare da mutane uku da za su tsaya mata.

 

Bayan haka, ya dage sauraron karar har zuwa ranar 13 ga Maris, domin ci gaba da Shari’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...