Majalisar dokokin Najeriya ta gayyaci shugabannin bankuna saboda karancin naira

Date:

Majalisar Dokokin Najeriya a ranar Talata ta gayyaci shuagabannin bankunan kasuwanci domin bayyana a gabanta a ranar Laraba kan karancin sabbin takardun kuɗi da ake fuskanta.

 

Babban Darekta kuma Shugaban Bankunan karkashin kwamitin bankuna, za su haɗu da kwamitin wucin gadi na Majalisar da shugaban masu rinjaye na majalisar Alhassan Ado-Doguwa ke jagoranta.

Talla

A wani zama da majalisar ta yi a yau Talata, ta yanke shawarar gayyato bankunan domin su zo gabanta su yi bayani kan matsalolin ƙarancin kuɗi da ake samu daga Babban Bankin Najeriya, inda daga baya za ta gayyato shugabannin na CBN domin zuwa amsa tambayoyi.

 

Majalisar ta kuma bukaci a tsawaita wa’adin amfani da tsoffin takardun kuɗi da wata shida.

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...