Majalisar dokokin Najeriya ta gayyaci shugabannin bankuna saboda karancin naira

Date:

Majalisar Dokokin Najeriya a ranar Talata ta gayyaci shuagabannin bankunan kasuwanci domin bayyana a gabanta a ranar Laraba kan karancin sabbin takardun kuɗi da ake fuskanta.

 

Babban Darekta kuma Shugaban Bankunan karkashin kwamitin bankuna, za su haɗu da kwamitin wucin gadi na Majalisar da shugaban masu rinjaye na majalisar Alhassan Ado-Doguwa ke jagoranta.

Talla

A wani zama da majalisar ta yi a yau Talata, ta yanke shawarar gayyato bankunan domin su zo gabanta su yi bayani kan matsalolin ƙarancin kuɗi da ake samu daga Babban Bankin Najeriya, inda daga baya za ta gayyato shugabannin na CBN domin zuwa amsa tambayoyi.

 

Majalisar ta kuma bukaci a tsawaita wa’adin amfani da tsoffin takardun kuɗi da wata shida.

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dr. Kabiru Getso Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Buhari

Daga Rahama Umar Gwaru   Tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli...

Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutu saboda rasuwar Buhari

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana Talata, 15 ga watan...

Injiniya Iliyasu Usman Salihu ya zama Jakadan zaman Lafiya na Africa

    Injiniya Ilyasu Uasman Salihu, Manajan Darakta na Sadex Engineering...

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...