Wani dan takarar majalisar wakilai a PDP ya rasu yana shirin fara kamfe

Date:

Daga Umar Sani Kofar Na’isa

 

 

Wani dan takarar majalisar wakilai a kananan hukumomin birnin Kebbi Kalgo da Bunza dake jihar Kebbi a jam’iyyar PDP Barr. Abba Bello Muhd ya rasu yana shirin fara fita yakin nema zaben kujerar da yake nema.

 

Dan takarar ya rasune a babban birnin tarayya Abuja bayan ‘yar gajeriyar jinya, ya rasu ne ya ana da shekaru 42 yana da mata daya da ‘yarsa guda daya.

 

Talla

Marigayi Barr. Abba Bello da ne ga tsohon Minista tsaro, kuma tsohon Ministan sadarwa na Nigeria Kuma tsohon shugaban jam’iyyar PDP na kasa Dr. Bello Halliru .

 

Kafin rasuwar sa a daren jiya juma’a shi ne wanda jam’iyyar PDP ta tsayar takarar Dan majalisar tarayya ya yankin Birnin Kebbi Kalgo da Bunza, ya kuma taba neman kujerar a shekara 2015 Amma Allah bai bashi nasara ba.

Talla

 

Rahotannin da kadaura24 ta samun sun nuna za dai ayi jana’izarsa a babban masallacin Abuja da misalin karfe 1 na ranar wannan Asabar din.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...