Muna cikin kyakyawan yanayin tsaro da za’a iya yin zabe – Gwamnan Borno

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya ce jihar Borno na da ingantaccen tsaro za a iya gudanar da zabukan 2023.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne yau Juma’a yayin ziyara ga shugaba Muhammadu Buhari a fadarsa da ke Abuja.

Talla

BBC Hausa ta rawaito Gwamna zulum ya tabbatar wa masu ‘yan jihar cewa za a basu cikakkiyar tsaro kafin da lokaci da kuma bayan zaɓe.

 

A baya-bayan nan ne ake nuna fargaba kan tsaro a jihar bayan da aka kai wa tawagar ƴakin neman zaɓen shugaban kasa na jam’iyyar PDP hari a Maiduguri a ranar 22 ga watan Nuwamba.

Talla

 

”Muna iyakar bakin kokarin mu a yanzu, muna shirye-shiryen sake mayar da mutane garuruwansu da kuma ganin yadda za mu sake gyara hanyar Maiduguri da Gamborun-Gala da kuma ta Maiduguri zuwa Banke da zimmar ganin mutane sun koma rayuwa kamar a baya,” in ji Gwamnan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku ba da gudunmawa kano ta zauna Lafiya – Waiya ya shawarci yan jaridun yanar gizo

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci kafafen yada labarai na...

KAROTA ta tabbatar da aniyarta na inganta matsayin jami’anta

Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano...

Sarkin Sanusi ya amince da nadin sabon mai unguwar Hotoro GRA

  Mai martaba Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi...