Sakacin Likita a asibitin Aminu Kano ya sa hannun wani jariri ya rube

Date:

Daga Auwalu Alhassan Kademi

 

 

Ana zargin wani likita a asibitin koyarwa na Aminu Kano da illata wani jariri ɗan kawanaki biyar.

 

Likitan dai ya bar tsirkiyar da ya ɗaure hannun jariri da ita yayin daukar jini har tsawon awanni 18.

 

Wanna ne ma ya jawo hannun yaro ke neman rubewa a halin yanzu.

Talla

binciken da wakilin Premier Radio ya gabatar ya gano cewa an yiwa mahaifiyar yaron aikine aka ciro shi daga cikinta.

 

Daga bisani likita ya ce yana fama da matsalar numfashi da hakan ta sa tilas aka kwantar dashi a bangare jarirai.

 

an kuma yi zargin cewa, awa 18 ba wani daga cikin jami’an lafiya a asibitin da ya kula yaron, balle ya lura da ɗaurin dake hannunsa, har sai da mahaifiyarsa taje bashi mama.

 

Talla

Tuni dai wasu likitoci suka ce sai dai a yanke hannun wanna jariri, sakamakon shafe tsahon lokaci jini bai gindaya ba.

 

Sai dai mahaifin yaron Malam Umaru Shamsu ya ce ma’aikatan asibitin na nuna masa wulakanci duk da dattakon da ya nuna.

 

Ya ce ya yi mamaki da aka kirashi wai yaje ya siyo maganin da za a baiwa ɗan nasa a ranar Litinin, duk da ɗanyen aikin da aka yi masa.

 

Kadaura24 ta tuntubi jami’ar hulda da jama’a ta Asibitin na Malam Aminu kano don jin yadda Akai aka haihu a ragawa, Amma ta ce mu bata lokacin zata bincika tare da sanar da mu abin da ta binciku, za dai mu cigaba da bibiyar lamarin.

 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...