Idan kuka zabe ni zan bunkasa tsaro da tattalin arziki kano – Tinubu

Date:

Daga Kamal Yakubu Ali

 

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Asiwaju Bola Ahmad Tinubu ya yi alkawarin bunkasa tsaro da harkokin tattalin arzikin jihar kano idan ya zama Shugaban Kasar Nigeria.

 

Bola Tinubu ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da malaman Arewa maso yammacin Nigeria a jihar Kano.

 

Talla

Yace kasancewar kano cibiyar Arewacin Nigeria akwai bukatar a bata kulawa ta musamman saboda idan ta bunkasa dukkanin jihohin Arewacin Nigeria sun bunkasa.

 

Bola Tinubu ya kuma yi alkawarin samar da wani tsari da zai taimaka wajen inganta harkokin karatun al-qur’ani saboda magance matsalar barace-barace a kasar nan.

 

Ya kuma yi alkawarin baiwa malamai dama a gwamnatin tarayya ta yadda za’a dama da su domin inganta kasar nan. Tinubu ya bukaci Malamai da su umarci dalibansu da sauran magoya bayansu da su zabe shi saboda yafi dukkanin yan takarar shugaban kasa chanchanta.

 

Talla

Da yake nasa jawabin gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya ƙalubalanci masu ganin baiken jam’iyyar APC don ta haɗa yan takarar shugaban kasa duk Musulmi, Inda yace haɗa Musulmi da Musulmi a takarar shugaban kasa ba sabon Abu bane a Ƙasar nan.

 

Ganduje ya kuma bada tabbacin cewa al’ummar Nigeria suna son jam’iyyar APC da yan takarar su Kuma zasu zabe su a babban zaben Mai zuwa .

 

Malamai da dama ne dai suka zo taron wadanda suka fito daga jihohin Arewacin Nigeria domin halartar taron wanda ke cikin jerin tarukan da aka tsara don yakin neman zaben Tinubu a kano.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...