Daga Khadija Abdullahi Aliyu
Mai Martaba Sarkin Kano Alh. Aminu Ado Bayero ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da mutunta shugabanni, sannan su yi amfani da kuri’unsu wajen zaben shugabanni na gari a lokacin zabe .
Sarkin ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Apc, Asiwaju bola Ahmad tunibu a fadar sa.

Cikin sanarwar da sakataren yada labaran Masarautar kano Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa kadaura24 yace Sarkin wanda ya bayyana Kano a matsayin cibiyar harkokin zabe ya yi kira ga jama’a da su yi amfani da kwarewarsu wajen zaben wadanda za su inganta rayuwar al’umma gaba daya.
Tun da farko dan takarar shugaban kasa Cif Bola Ahmad Tunibu ya ce ya zo jihar Kano ne domin kaddamar da yakin neman zabensa a Arewa maso Yamma kuma ya nemi addu’ar Sarkin da kuma al’ummar jihar.

A yayin ziyarar dan takarar shugaban kasa Bola Ahmad Tunibu ya samu rakiyar gwamnan jihar Dr. Abdullahi umar Ganduje, da mataimakinsa Dr. Nasiru yusif Gawuna, gwamnan jihar Zamfara, Sanata barau jibrin, shugaban jam’iyyar na jiha Abdullahi Abbas, tsofaffin gwamnoni, da manyan jami’an gwamnatin tarayya.