Babu wani shiri na karin albashin ma’aikata a 2023 – Gwamnatin tarayya

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Gwamnatin Tarayya, a ranar Juma’a ta ce ba wani shiri da take yi na karawa ma’aikatan ta Albashi kamar yadda aka ruwaito a wasu jaridun kasar nan suka rawaito kwanakin baya, inda ta ce wasu “alawus-alawus na musamman” ne kawai take shirin karawa .

 

 

Ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Chris Ngige, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da kakakin ma’aikatar, Olajide Oshundun ya fitar, inda ya jaddada cewa babu batun sake yiwa ma’aikata karin Albashi.

Talla

 

Ngige, yayin da yake zantawa da manema labarai a fadar gwamnatin jihar a ranar Talata, ya ce kwamitin da shugaban kasa ya kafa kan albashin ma’aikata na yin nazari, kuma ana sa ran zai fito da tsarin daidaita albashin a sabuwar shekara.

 

Tallan Garin dan wake mai inganci

Sai dai ministan a ranar Juma’ar nan ya ce Ngige ya ce karin da ya yi magana a kai shi kan alawus din wasu ma’aikatan na musamman ba wai karin Albashi ba, inda ya kara da cewa har yanzu ana kan aiki.

 

 

Sanarwar ta kara da cewa, “Kwamitin shugaban kasa kan albashi (PCS) ta ofishin sakataren gwamnatin tarayya (OSGF) ya karbi shawarwarin duba alawus-alawus na ma’aikatu da hukumomin gwamnati da dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...