A shirye muke mu taimaka don inganta aiyukan yan Hisbah a Kaduna – Kwamandan Hisbah na Kano

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Kwamandan Hukumar hisbah ta jihar Kano Sheikh Harun Muhammad Sani Ibn Sina ya ce hukumar zata cigaba da aiki da Takwararta ta jihar Kaduna domin Dabbaka harkokin Addinin Musulunci.

Sheikh Muhammad Sani Ibn Sina ne ya bayyana hakan a ziyarar aiki da ya kaiwa takwaransa a Kaduna.
Haroon Ibn Sina wanda mataimakinsa a bangaren horarwa Malam Idris ibn Umar ya wakilta ya ce babbar nasara ce da hukumar a jihar Kaduna ta samar da Dakarunta a Zaria da kewaye domin zai tallafa wajen yaki da Badala da kuma aikata bai dai-dai ba a jihar.
Talla
Ibn Umar ya ce kofar hukumar Hisbah ta jihar Kano a bude yake wajen neman shawara da goyon baya ko horarwa a duk lokacin da bukatar hakan ta taso.
Malam ibn Umar ya ce adadin sababbin dakarun su 75 a zazzau zai taimakawa hukumar kwarai da gaske wajen gudanar da ayyukan ta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...