A shirye muke mu taimaka don inganta aiyukan yan Hisbah a Kaduna – Kwamandan Hisbah na Kano

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Kwamandan Hukumar hisbah ta jihar Kano Sheikh Harun Muhammad Sani Ibn Sina ya ce hukumar zata cigaba da aiki da Takwararta ta jihar Kaduna domin Dabbaka harkokin Addinin Musulunci.

Sheikh Muhammad Sani Ibn Sina ne ya bayyana hakan a ziyarar aiki da ya kaiwa takwaransa a Kaduna.
Haroon Ibn Sina wanda mataimakinsa a bangaren horarwa Malam Idris ibn Umar ya wakilta ya ce babbar nasara ce da hukumar a jihar Kaduna ta samar da Dakarunta a Zaria da kewaye domin zai tallafa wajen yaki da Badala da kuma aikata bai dai-dai ba a jihar.
Talla
Ibn Umar ya ce kofar hukumar Hisbah ta jihar Kano a bude yake wajen neman shawara da goyon baya ko horarwa a duk lokacin da bukatar hakan ta taso.
Malam ibn Umar ya ce adadin sababbin dakarun su 75 a zazzau zai taimakawa hukumar kwarai da gaske wajen gudanar da ayyukan ta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku ba da gudunmawa kano ta zauna Lafiya – Waiya ya shawarci yan jaridun yanar gizo

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci kafafen yada labarai na...

KAROTA ta tabbatar da aniyarta na inganta matsayin jami’anta

Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano...

Sarkin Sanusi ya amince da nadin sabon mai unguwar Hotoro GRA

  Mai martaba Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi...