Nan da makonni 6 za’a bude tashar wutar lantarki ta kano – Ganduje

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamnatin jihar kano tace zata bude Sabuwar Tashar samar da wutar Lantarki mai Karfin Megawatts 10.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje yace anasa ran nan da mako 6 za ai bikin kadammar da Tashar da take Tiga.
Talla
Anasa ran tashar zata samar da wuta mai Karfin KV 33 ga Tashar Ruwa ta Tamburawa da Kuma Haskaka Titunan Jihar Kano.
Wani sashi na tashar wutar
Yayin da ya ziyarci Inda ake aikin wutar dake garin Tiga, Gwamna Ganduje yace ya gamsu da ingancin aikin da aka gudanar a wajen, Inda ya yabawa hukumar kula da wutar lantarki ta jihar kano bisa kokarin da suke don tabbatuwar aikin.
Tini dai gwamnatin jihar kano ta sanarwa da tashoshin wutar lantarkin lasisin fara aikin tun a watan Yuni na shekara ta 2021 daga hukuma dake bada lasisin don fara aiki gadan-gadan.
Wani sashi na tashar wutar lantarkin
Ganduje ya bada tabbacin zai cigaba da gudanar da aiyukan da zasu inganta rayuwar al’ummar jihar kano gabanin karewar wa’adin mulkin sa, don barwa al’ummar Kano abun da zasu dade suna tunawa da shi .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...