Bana Jin dadin yadda wasu suke kirana da Jibrin dan Sudan – Buhari

Date:

Daga Maryam Abubakar Tukur

 

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce iƙirarin da wasu ke yaɗawa cewa wani mutum ne mai suna Jubril daga Sudan yake mulkin Najeriya ba abin dariya ba ne kuma an ƙirƙire shi ne don kawar da hankalin gwamnatinsa.

 

Buhari ya bayyana haka ne cikin wani fim kan rayuwarsa da aka haska yayin bikin cikarsa shekara 80 da haihuwa na musamman da aka yi a Abuja.

 

Talla

Shugaban na mayar da martani ne ga wani shaci-faɗin da aka fara yaɗawa daf da ƙarewar wa’adinsa na farko a kan mulki cewa ya rasu amma wani mutum mai suna Jubril daga Sudan ne ya maye gurbinsa a Fadar Shugaban Ƙasa Aso Rock.

 

Ya ce masu ta da zaune tsaye ne suka ƙirƙiri maganar “saboda wulaƙanci”.

 

A cewarsa: “A’a, ba abin dariya ba ne saboda waɗanda suka ƙirƙiri zancen sun yi ne saboda wulaƙanci. Suna so su karkatar da hankalin gwamnati daga kan muhimman abubuwa.

 

“Babbar manufarmu ita ce yin ayyukan raya ƙasa, mu fargar da mutane su san cewa akwai buƙatar su yi aiki tuƙuru don su rayu cikin walwala.

 

“Suna [masu yaɗa iƙirarin] son su ji daɗin rayuwa ne kawai da kuma samun goyon bayan al’ummarsu.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...