Rashin tsaro: Zan Ninka Adadin ‘yan sanda, Sojoji, DSS a Nigeria idan na zama shugaban kasa– Kwankwaso

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

 

Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigerian People Party (NNPP) a karshen makon nan ya yi alkawarin kara yawan jami’an tsaron Najeriya da kashi 400 idan har aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a shekarar 2023.

Kwankwaso wanda ya yi magana a Dutse, babban birnin jihar Jigawa ya bayyana cewa adadin jami’an tsaro a halin yanzu yayi kadan .

Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso ya ce “adadin ‘yan sandan Najeriya, sojoji, jami’an tsaron farin kaya da jami’an tsaron na civil defense da duk wasu jami’ai dake damara ba su da yawan da zasu magance matsalolin da tsaron da kasar nan take fuskanta”.

 

Talla

A cewarsa “idan aka yi la’akari da yawan al’ummar Najeriya kuma idan aka kwatanta da yawan jami’an tsaro, babu yadda za a yi su magance aikata laifuka da Najeriya”.

“In Allah ya yarda idan na zama shugaban Najeriya, zan ninka adadin ‘yan sanda, Sojoji, jami’an tsaron farin kaya DSS da dai sauransu da kashi 400 cikin 100”, in ji Kwankwaso.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...