Akwai yiwuwar darajar naira ta sake faɗuwa a ƙarshen shekara

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

 

Masana harkokin sauyin kuɗi a Najeriya na ganin darajar kuɗin ƙasar naira za ta sake faɗuwa yayin da shekarar 2022 ke ƙarewa, musamman a farashin gwamnati.

 

An canzar da dala ɗaya kan N457 a farashin gwamnati ranar Alhamis, fiye da N450 da aka canzar da ita a makon da ya gabata.

 

A kasuwar bayan fage kuwa an canzar da dalar kan N740.

 

Talla

“Shekara ta zo ƙarshe…ba na tsammanin za ta farfaɗo,” a cewar wani ɗan kasuwa a bankin kasuwanci cikin hirarsa da Reuters. “Amma ina ganin za ta zauna yadda take ko ta ɗan faɗi kaɗan.”

 

Sauya wasu takardun naira a watan nan da kuma rage adadin kuɗin da ɗaiɗaikun mutane da kamfanoni za su iya cirewa a kullum na ci gaba da ɗumama harkokin kuɗi a Najeriya.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...