Mun kashe ‘yan Boko Haram 103, in ji Rundunar Sojan Najeriya

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Rundunar Sojan Najeriya ta ce dakarunta sun kashe mayaƙan ƙungiyar Boko Haram da na ISWAP 103 cikin mako uku da suka gabata.

Wata sanarwa da rundunar ta fitar ta ce dakarun rundunar Operation Hadin Kai ne suka kashe masu iƙirarin jihadin a yankin arewa maso gabashin ƙasar.

Kazalika, ta ce ta kama ‘yan ta’adda 22 da masu taimaka musu 18 yayin samamen da ta kai a wannan tsakanin.

Talla

Shekarar 2022 ta zo wa ƙungiyoyin da asara iri-iri, musamman shugabanninsu da aka kashe a Gabas ta Tsakiya da Afirka ta Yamma.

Sai dai su ma sun ƙaddamar da munanan hare-hare kan gidan yari, musamman na Kuje a Abujar Najeriya, inda ISWAP ta fitar da mayaƙanta da kuma ɗaruruwan tsararru.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...