Kada ku bari talaucin da ake ciki a Nigeria yasa ku sayar da kuri’unku – Falakin Shinkafi

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Wani masarake kuma dan kishin kasa Amb. Dr. Yunusa Yusuf Hamza Falakin Shinkafi ya yi kira ga al’ummar Nigeria da su guji sayar da kuri’unsu yayin babban zaben shekara 2023 dake tafe.

 

  • “Babu shakka ana fama da talauci, amma bai kamata ya zama dalilin da zai sa al’ummar Nigeria su sayar da kuri’unsu ga gurbatattun shugabanni ba”. Inji Falakin Shinkafi

 

Amb. Dr. Yunusa Yusuf ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi da shirin Demokaradiyya adon kasa na gidan Radion Nigeria Kaduna.

Talla

Yace duk da irin matakan da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta dauka domin dagile magudin zabe a bana, Amma har yanzu wasu yan siyasar sun tara magudan kuɗade domin baiwa talakawa don su zabe su.

 

Falakin Shinkafi wanda ya shahara wajen tallafawa matasa yace kamata yayi yan Nigeria su dubi chanchanta lokaci zabe, saboda zabar Shugaba nagari shi ne zai sa a sami saukin tarin matsalolin da ake fuskanta a kasar nan.

 

  • ” Duk wanda zai baka kudi don ka zabe shi to ka sani idan yaci zaben sai ya mayar da kudaden daya baku idan ma zai yi muku wani abun kirki, Amma idan chanchanta kuka bi to wlh kun tsira har a gurin Allah”.

” Ni a Sani na ban taba ganin an sayi kuri’u da kudin da suka taka Kara suka karya ba, a baka dubu da Kuma kaje asibiti ko ka kai matarka ko ‘ya’yanka ka kashe sama da gubu 50 me gari ya waya, kuma kaje ka fadawa Allah dalilin da yasa ka yi haka”. Inji Falakin Shinkafi

Daga ƙarshe yayi fatan Samun shugabanni nagari wadanda zasu taimaka wajen fitar da al’ummar Nigeria daga cikin mawuyacin halin da suke ciki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...