2023: Zunzurutun Yan Bokon Kura Madobi da Garun Mallam Sun yi Alkawarin Marawa Musa Iliyasu baya – Com. Mukhtar

Date:

Daga Yakubu Abubakar Gwagwarwa

 

Zunzurutun yan boko a yankin kura madobi da garun Mallam sun bayyana goyon bayan su ga dan takarar majalisar tarayya na jam’iyyar APC Hon. Dr. Musa Iliyasu Kwankwaso a zaben shakara ta 2023 dake tafe.

 

Shugaban gamayyar kungiyoyin dalibai da sauran yan bokon dake yankin Kwamaret Mukhtar, ne ya bayyana hakan yayin wani taron nuna goyon baya ga Musa Iliyasu Kwankwaso, wanda ya gudana a dakin taro na Sani Abacha Youths center a kano.

 

Kwamaret Mukhtar yace zasu goyawa Musa Iliyasu Kwankwaso baya ne saboda yadda a baya ya rika tallafawa daliban yankin da kudin tallafin karatun da sauran tallafi kan abun da ya shafi karatun su.

 

” Wannan kungiyar ta zunzurutun yan boko ce dake kura madobi da garun Mallam, mun yanke shawarar marawa Musa Iliyasu bayan ne saboda duk wani dan boko yaci Arzikin musa, ko kai tsare ko kuma ba ta kai tsaye ba, don haka muka ga dacewar Saka alkhairi da alkhairi”.

Talla

 

” Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso wadannan matasa da kake gani wakilcin kawai suka zo don jaddada goyon bayan mu ga takarar ka saboda muna da kyakyawan yaƙinin idan Allah ya baka wanann damar zaka tallafawa harkokin ilimi da sauran fannoni a yankin mu”. Inji Kwamaret Mukhtar

 

Shugaban gamayyar kungiyoyin ya Sha alwashin zasu koma mazabun su domin cigaba da wayar da kan al’umma maza da matasa muhimmancin zabar Musa Iliyasu Kwankwaso a matsayin dan majalisar tarayya, da Kuma irin alfanun da kowa zai samu idan Musa Iliyasu yaje majalisar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...