Zan raba tallafin karatun digiri a jami’ar NOUN ga ɗalibai 220 kafin zaɓe — Sha’aban Sharada

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

 

Ɗan takarar gwamna a jihar Kano, ƙarƙashin jam’iyyar ADP, Sha’aban Sharada ya yi alkawarin ɗaukar nauyin karatun digiri na dalibai, ƴan asalin jihar a jami’ar karatu da ga gida, wato National Open University (NOUN).

 

Sharada, ɗan majalisar wakilai mai wakilta

Talla

r Kano Municipal, ya yi wannan alkawari ne a shafinsa na Twitter a ranar Juma’a.

 

 

Saharada ya yi alƙawarin ɗaukar nauyin ɗalibai 5 daga ko wacce Ƙaramar Hukuma, a cikin ƙananan hukumomi 44 na jihar Kano, inda adadinsu ya kai 220 kenan.

 

Ya kuma yi alƙawarin aiwatar da wannan aiki kafin zaɓen 2023.

 

“Kafin zabe, Zan Dauki Nauyin Karatun Dalibai biyar (5) a kowacce Karamar Hukuma (44) na Jahar Kano har su Gama Degree na farko a National Open University…5×44 = 220 Students,” in ji Sharada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...