Daga Ibrahim Sani Gama
Al’ummar garin sabon bakin kunza ta Nasarawan kofa dake karamar hukumar Bebeji sun yabawa Hakimin bebeji Majidadin Rano Alh Tijjani Abdullahi, bisa kokarin da ya yiwa al’ummar unguwar Nasarawan kofa na Samar musu da ginin makaranta, saboda doguwar tafiyar da ‘yayensu suke yi a lokutan baya domin Neman ilimi.
Shugaban al’ummar yankin malam Ibrahim wada bebeji, Wanda yayi jawabi a madadin al’ummar garin ne ya bayyana haka a wata zantawa da manema labarai.
“Muna mika godiyarmu ga hakimin da sakataren ilimin karamar hukumar ta bebeji saboda gudunmawar da suka bayar wajen samun Wannan makarantar wadda Ina yi Imani zata taimaka matuka wajen inganta Rayuwar matasan mu baki daya “. Inji Wada

Ibrahim wada bebeji, yace a lokutan baya, yaran Nasarawar kofa suna yin tafiyar kilomita uku domin zuwa neman ilimi, amma sakamakon gina wannan makaranta yanzu ba sai sun tafi wani guri ba, inda yace,wannan ba karamar nasara bace, ga al’ummar yankin da karamar hukumar bebeji baki daya.
Ya kuma yi kira ga masu ruwa da tsaki a yankin da masu hannu da shuni da su tallafawa unguwar nasarawan kofa, musamman yan siyasa da su samarwa yankin makarantun da ‘yayensu za su rika zuwa domin neman ilimi addini da na Zamani don kara inganta Rayuwar al’ummar yankin.
Shin Yan adaidaita sahu sun bi sabuwar dokar hana su hawa manyan titunan Kano kuwa ?
Ya kara da cewa rashin zuwan yara makaranta a halin yanzu ba karamar Matsala bace, Inda yace hakan aka jawo a samun batagari a cikin al’umma, wanda kuma hakan barazana ce ga tsaron lafiya da dukiyoyin al’ummar yankin.
Ibrahim wada bebeji, yayi kira ga Gwamnati, musamman ta karamar hukumar su, da ta taimakawa wannan yankunan da Karin makarantu kasancewar suna da karanci makarantun da ‘ya’yansu za su rika zuwa neman ilimi domin kaucewa shiga wasu matsalolin da ka iya tasowa a yankunan na karamar hukumar ta bebeji.
Yace,yanzu ne ya kamata a baiwa wannan yankunan tallafi da agajin da suka kamata,domin su ma su kurbi romon damaradiyya,ta hanyar nemawa ‘yayensu mafita domin ilimi shine gishirin rayuwa da ci gaban alumma a kodayaushe.