Mamallakan jiragen kansu a Najeriya sun maka gwamnati kotu

Date:

Daga Maryam Abubakar Tukur

Masu jiragen sama na kashin kansu a Najeriya sun yanko wa gwamnati sammaci, inda su ke bukatar kotu ta hana ta dakatar da jiragen nasu tashi saboda kin biyan kudin fito.

A watan Nuwamban bara ne hukumar hana fasa kwauri ta kulle jirage 91 mallakar wasu hamshakan masu arziki a kasar, bisa zargin kin biyan kudaden fito da yawansu ya haura naira biliyan 30.

Talla

Hukumar ta kwastam ta samu sahalewa daga ofishin Shugaban kasa, na umurtar masu ruwa da tsaki a harkar sufurin jiragen sama na hana jiragen daidaiku da ake bi bashin kudin fito aiki.

Sai dai jaridar Punch ta cikin gida ta ruwaito cewa mamallakan jiragen na neman kotu ta sake duba halaccin tursasa musu biyan kudin fiton, kamar yadda hukumar kwastam din ke ikirari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...