Shin Yan adaidaita sahu sun bi sabuwar dokar hana su hawa manyan titunan Kano kuwa ? 

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi
Matuka baburan adaidaita sahu a jihar kano su bi dokar da gwamnatin jihar kano ta dora musu ta hana su bin wasu manyan titunan jihar.
Kadaura24 ta rawaito tun daren litinin din data gabata ne gwamnatin jihar kano ta karkashin hukumar Karota ta bada sanarwar dakatar da yan adaidaita sahun daga bin wasu manyan tituna a Kano.
Talla
Binciken da jaridar kadaura24 ta gudanar ya nuna cewa yan adaidaita sahun sun bi waccen doka, domin kuwa sun ƙauracewa titunan da aka ce ba’a son ganin su akai, wadanda suka hadar da tituna Ahmad Bello way by Mundubawa da Kuma tal’udu zuwa gwarzo.
Wakilin mu ya shaida yadda aka jibge jami’an hukumar karota domin ganin sun tabbatar da ba Wani dan adaidaita sahu da ya karya dokar.
Gwamnatin kano dai tuni ta samar da manyan motocin safa-safa domin maye gurbin yan adaidaita sahun da su a kokarin ta na Kara inganta harkokin sufuri a kano, haka Kuma gwamnatin ta yi alkawarin karo wasu motocin domin sanyasu a sauran manyan titunan jihar kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...