Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta dora alhakin katutun talaucin da ke damun kasar kan gwamnonin jihohi.
Karamin Ministan Kasafin Kudi da Tsare-Tsare, Clem Agba ne ya bayyana hakan ga manema labarai bayan taron majalisar zartarwa ta tarayya ranar Laraba, kamar yadda gidan talbijin na Channels TV ya rawaito.

Ya ce shirin gwamnatin tarayya na kyautata rayuwar ‘yan kasar bai yi tasirin da ya kamata ba ne saboda gwamnonin jihohi ba su bai wa gwamnatin tarayya hadin kai ba.
Mr Agba ya kara da cewa gwamnonin sun fi mayar da hankali wajen aiwatar da ayyukan da ba su da muhimmanci, maimakon inganta rayuwar al’ummar karkara.