Yan adaidaita sahu: Gwamnatin Kano ta magantu kan wahalar da mutan kano suka sha

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Mataimakin gwamnan jihar kano Dr Nasiru Yusuf Gawuna yace nan da jimawa kadan zata zauna domin sake yin duba kan sabuwar dokar hana yan adaidaita sahu bin wasu manyan tituna a Kano .

 

Talla

Mun sami labarin halin da al’umma suka shiga sakamakon Wannan doka, yanzu haka gwamnati ta bada dama a sake duba dokar don samar da abun da bazai musgunawa al’umma ba”. 

 

Mataimakin gwaman ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya fitar a yammacin ranar larabar nan.

 

Yace gwamnati ta tura jami’ai domin duba halin da al’umma suka shiga, Kuma ta ji koke -koken al’umma, zata ɗauki matakan saukakawa al’umma tunda dama gwamnatin ta al’umma ce .

 

” Duk abun da ya kamata a yi in Allah ya so nan da zuwa an jima kadan gwamnati ta sahale mu zauna mu duba mu gani, domin a kawo masalahar Wannan al’amarin, Kuma Ina tabbatarwa al’umma cewa bi’izinin lahi za’a yi abun da al’umma zasu ji dadin sa”. Inji Gawuna 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...