Wata babbar mota ta hallaka jami’an Road Safety 2

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Wani direban babbar mota ya kashe jami’an Hukumar Kiyaye Aukuwar Hadura ta Najeriya biyu a kan babbar hanyar Aba da ke kudancin ƙasar.

 

A wata sanarwa da hukumar ta fitar mai ɗauke da sannun babban jami’in wayar da kan jama’a na hukumar Bisi Kazeem, ya ce muƙaddashin babban shugaban Hukumar Dauda Ali Biu, ya bayyana damuwarsa game da kashe jami’an hukumar biyu, tare da alkawarta gurfanar da waɗanda suka yi sanadiyyar mutuwar jami’an a gaban kotu domin su fuskanci hukunci .

 

Talla

Sanarwa ta ce Mista Biu ya yi Allah wadai da wannan lamari da ya yi sanadiyyar mutuwar jami’an hukumar waɗanda ke bakin aikinsu, sakamakon abin da ya kira ‘aikin direbobi masu tukin ganganci waɗanda ke ci gaba da karya dokar tuƙi’

An sace kayan fitar angwanci na wani ango a Kano

Lamarin ya faru ne sakamakon ƙoƙarin kauce wa rami da direban babbar motar ya yi, yayin da yake tsaka da gudu a kan hanyar, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

 

Jami’an hukumar FRSC dai sun daɗe suna zargin direbobin ƙasar da tukin ganganci tare da gudun wuce kima a kan titunan ƙasar, lamarin da hukumar ke cewa shi ne musabbabin mafi yawancin haduran da ke aukuwa a kan titunan ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...