2023: Gwamna Badaru ya mika tutoci ga yan takarar APC na shiyyar Gumel

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Gwamnan jihar Jigawa Alhaji Mohammad Badaru Abubakar MON, mni ya mika tutoci jam’iyyar APC ga ‘yan takarar Santoriyar Jigawa ta arewa maso yamma wato shiyyar Gumel.

 

Dubban magoya bayan jam’iyyar da manyan ‘ya’yan jam’iyyar na daga cikin wadanda suka halarci taron wanda ya gudana a karamar hukumar Gumel ta jihar.

 

Da yake jawabi ga magoya bayansa, Gwamna Badaru Abubakar ya bukaci al’ummar jihar Jigawa da su zabi jam’iyyar APC daga sama har kasa, domin a cewarsa jam’iyyar ta samar da dimokuradiyya ga al’ummar jihar.

Talla

Cikin sanarwar da kwamishinan aiyuka na musamman na jihar Jigawa Hon. Auwalu Danladi Sankara ya fitar ta sahihin shafinsa na Facebook, yace gwamnan  ya kara da cewa jam’iyyar APC za ta ci gaba da ba da fifiko a bangaren ilimi, lafiya, samar da ababen more rayuwa, da karfafa tattalin arziki.

 

Dan takarar gwamnan jihar Alhaji Umar Namadi wanda kuma shi ne mataimakin gwamnan jihar ya tabbatarwa al’ummar jihar Jigawa cewa zai dora kan aiyukan cigaba ga gwamnan Badaru ya faru domin cigaban jihar idan har al’ummar jihar suka zabe shi matsayin Gwamnan Jigawa.

 

A cewar dan modi, gadon gwamnan jihar Jigawa Alhaji Mohammed Badaru Abubakar bai dace ga rago ba wadanda basu San daga Inda aka taho ba da Inda za’a kai jihar Jigawa, ta bangarorin lafiya, aikin noma, Samar da aiyukan yi ga matasa maza da mata da Samar da ababen more Rayuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...