Gobara ta hallaka Mutane Uku a Kano

Date:

Daga Maryam Abubakar Tukur

 

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da mutuwar wasu ‘yan uwa guda uku sakamakon wata gobara da ta tashi a Kabuga Yan Azara da ke karamar hukumar Gwale.

 

Da yake bayyana lamarin, jami’in hulda da jama’a na hukumar, PFS Saminu Yusif Abdullahi ya bayyana cewa gobarar da ta hada da wani bene ta faru ne a daren ranar Litinin.

 

Talla

Ya kara da cewa, gobarar ta tashi daga saman ginin ta yi sanadiyyar mutuwar wasu ‘yan uwa uku Saddiqa Salisu ‘yar shekara 6, Abdulsamad mai shekaru 15 da kuma ‘yar uwarsu Fatima Isiyaku.

 

Saminu Yusif ya yi nuni da cewa, gobarar ta laso wasu sassan ginin, sakamakon kasa sanar da hukumar kashe gobara ta jihar Kano a kan lokaci.

 

Ya kuma bukaci jama’a da su rika kula sosai tare da sanar da hukumar akan lokaci domin rage yawan asarar da za’a yi .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...