Gobara ta hallaka Mutane Uku a Kano

Date:

Daga Maryam Abubakar Tukur

 

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da mutuwar wasu ‘yan uwa guda uku sakamakon wata gobara da ta tashi a Kabuga Yan Azara da ke karamar hukumar Gwale.

 

Da yake bayyana lamarin, jami’in hulda da jama’a na hukumar, PFS Saminu Yusif Abdullahi ya bayyana cewa gobarar da ta hada da wani bene ta faru ne a daren ranar Litinin.

 

Talla

Ya kara da cewa, gobarar ta tashi daga saman ginin ta yi sanadiyyar mutuwar wasu ‘yan uwa uku Saddiqa Salisu ‘yar shekara 6, Abdulsamad mai shekaru 15 da kuma ‘yar uwarsu Fatima Isiyaku.

 

Saminu Yusif ya yi nuni da cewa, gobarar ta laso wasu sassan ginin, sakamakon kasa sanar da hukumar kashe gobara ta jihar Kano a kan lokaci.

 

Ya kuma bukaci jama’a da su rika kula sosai tare da sanar da hukumar akan lokaci domin rage yawan asarar da za’a yi .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...