Ba ruwana da Social media saboda jini na yana hawa idan naga ana zagina– Tinubu

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Asiwaju Bola Tinubu, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, ya ce ya daina karanta shafukan sada zumunta saboda suna sawa jini na ya hau.

 

Tinubu ya bayyana hakan ne a cikin wani faifan bidiyo da kadaura24 ta gani yayin wani taro.

 

 “ Na dai na karanta kafafen sada zumunta, saboda suna zagi da cin mutunci na, Idan na karanta raina yana baci kuma jini na ya hawa don haka na daina tuba ta. Idan ina son Jin wani abun ya’yana ko ma’aikata na su kan fada min .” Inji Tinubu

 

Talla

Yayin da yake karkare jawabinsa a gangamin yakin neman zabensa da aka gudanar a Jos a ranar Talata, ya sha fama da zamiyar harshe yayin da ya yi kuskuren cewa jam’iyyar PDP a lokacin da ya ke tunanin jam’iyyarsa ta APC.

 

Hakan dai ya jawo cece-ku-ce a shafukan sada zumunta yayin da masu suka suka yi wa dan takarar jam’iyya mai mulki suka ce bai cancanci zama shugaban kasa ba.

 

Masu sukar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC ta yanar gizo sun ce Tinubu ya kaucewa muhawara domin kada a yi ta tafka magudi

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...